04/09/2026
Rasuwar Sarkin Gumel Babban Rashi ce ga Masarautun Gargajiya da Nijeriya – Kashim Shettima
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, CON, a matsayin babban rashi ga Jihar Jigawa da Nijeriya baki ɗaya.
Shettima ya ce marigayi Sarkin ya kasance daga cikin sarakunan gargajiya da s**a sadaukar da shekaru masu yawa wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ilimi, ci gaban al’umma da ƙarfafa haɗin kan ƴan ƙasa.
Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a Jihar Jigawa, lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayin da Masarautar Gumel, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin tarayya.
Marigayi Sarkin Gumel na 16 ya rasu a birnin Alkahira na ƙasar Masar a ranar 3 ga Satumba, 2026, bayan shafe kusan shekaru 46 yana mulkin masarautar. Ya hau karagar mulki ne a ranar 16 ga Disamba, 1980.
Mataimakin Shugaban Ƙasan ya ce za a tuna da marigayi Sarkin ne saboda tsawon mulkinsa, tare da hikima, zaman lafiya da kishin al’ummar da ya nuna wajen gudanar da shugabancinsa.
Ya bayyana shi a matsayin uba, mai haɗa kan jama’a, kuma mai bayar da shawarwari, wanda hikimarsa ta taimaka wajen hidimtawa al’umma da ƙasa tsawon kusan rabin ƙarni.
Shettima ya ce duk da cewa mulkin marigayin ya gudana a lokacin da Nijeriya ta fuskanci sauye-sauyen siyasa da zamantakewa da dama, ya ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, ilimi, karatun addinin Musulunci da zaman tare cikin lumana.
Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama marigayi Sarkin, musamman bisa gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma.
Shettima ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi, tare da ba iyalansa, Masarautar Gumel da al’ummar Jihar Jigawa haƙurin jure wannan babban rashi.Najeriya da São Tomé za su ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu — Matawalle
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Shugaban Ƙasar São Tomé da Príncipe, Carlos Manuel Vila Nova, murnar sake zaɓensa, tare da neman ƙarfafa haɗin gwiwar ƙasashen biyu a fannonin tsaron teku, Yankin Haɗin Gwiwa na Ci Gaban Najeriya da São Tomé, kasuwanci da zuba jari.
Tinubu, wanda Ministan Ƙasa na Tsaro, Bello Matawalle, ya wakilta, ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a birnin São Tomé, yayin bikin rantsar da Vila Nova a wa’adinsa na biyu na shekaru biyar.
Vila Nova ya samu kashi 55.88 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa a zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasar São Tomé da Príncipe da aka gudanar a ranar 19 ga Yuli.
A cikin wasiƙar taya murnar da aka miƙa wa Vila Nova, Tinubu ya ce nasarar tasa ta nuna irin amincewar da al’ummar São Tomé s**a yi da jagorancinsa.
“Mai girma Shugaba, a madadin Gwamnati da al’ummar Tarayyar Najeriya, ina taya ku murnar sake zaɓenku a matsayin Shugaban Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar São Tomé da Príncipe,” in ji Tinubu.
Shugaban ya yaba wa gwamnatin São Tomé, Hukumar Zaɓe ta ƙasar, jam’iyyun siyasa da al’ummar ƙasar bisa gudanar da zaɓen cikin lumana, sahihanci da gaskiya.
Ya ce yadda aka gudanar da zaɓen zai ƙara ƙarfafa cibiyoyin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Tinubu ya ce Najeriya na matuƙar daraja kyakkyawar dangantakar da ta daɗe tana tsakanin ƙasashen biyu.
“Saboda haka, ina fatan ƙara zurfafa haɗin gwiwa a fannonin tsaron teku, Yankin Haɗin Gwiwa na Ci Gaban Najeriya da São Tomé da Príncipe, kasuwanci da zuba jari, da sauran fannoni da ke da muhimmanci ga ƙasashenmu,” in ji shi.
Matawalle ya isa filin jirgin sama na Nuno Xavier Dias International Airport da ke São Tomé a yammacin Laraba, domin wakiltar Shugaba Tinubu a bikin rantsarwar.
An gudanar da bikin ne a ginin Majalisar Dokokin ƙasar, inda shugabannin ƙasashen Afirka da Turai da sauran manyan baki s**a halarta.
Daga cikin waɗanda s**a halarci bikin akwai Shugaban Jamhuriyar Congo, Denis Sassou Nguesso; Shugaban Gabon, Brice Oligui Nguema; da Firaministar Mozambique, Maria Benvinda Levy.
Haka kuma, Ministan Harkokin Wajen Angola, Téte António, wanda ya wakilci Shugaban ƙasar; Firaministan Morocco, Aziz Akhannouch; da Firaministan Portugal, Luís Montenegro, na daga cikin mahalarta.
Tsoffin shugabannin São Tomé da Príncipe da Firaministan ƙasar, Américo Ramos, su ma sun halarci bikin rantsarwar.
Matawalle ya isar da saƙon fatan alheri daga Tinubu ga Vila Nova, tare da sake tabbatar da aniyar Najeriya na ƙara ƙarfafa dangantaka da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu.